Menu

Zabura 52

BIB

1 Me ya sa kake fariya game da mugunta, kai babban mutum? Me ya sa kake fariya dukan yini, kai da kake abin kunya a idanun Allah?

2 Harshenka kan shirya hallaka; yana nan kamar reza mai ci, kana ta ruɗu.

3 Kana ƙaunar mugunta fiye da alheri, ƙarya a maimakon faɗin gaskiya. Sela

4 Kana ƙaunar kowace kalmar cutarwa, Ya kai harshe mai ruɗu!

5 Tabbatacce Allah zai kai ka ga madawwamiyar hallaka. Zai fizge ka yă yayyage ka daga tentinka; zai tumɓuke ka daga ƙasar masu rai. Sela

6 Masu adalci za su ga su ji tsoro; za su yi masa dariya, suna cewa,

7 “Yanzu, ga mutumin da bai mai da Allah mafakarsa ba amma ya dogara a yawan arzikinsa ya kuma yi ƙarfi ta wurin hallaka waɗansu!”

8 Amma ni kamar itace zaitun ne ina haɓaka a gidan Allah; na dogara ga ƙauna marar ƙarewa ta Allah har abada abadin.

9 Zan yabe ka har abada game da abin da ka yi; a cikin sunanka zan dogara, gama sunanka yana da kyau. Zan yabe ka a gaban tsarkakanka.

Everything we make is available for free because of a generous community of supporters.

Donate