Menu

Zabura 114

BIB

1 Sa’ad da Isra’ila ya fito daga Masar, gidan Yaƙub daga mutane masu baƙon harshe,

2 Yahuda ya zama wuri mai tsarki na Allah, Isra’ila mallakarsa.

3 Teku ya kalla ya kuma gudu, Urdun ya juye da baya;

4 duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai kamar tumaki.

5 Me ya sa, ya teku, kika gudu, Ya Urdun, ka juya baya,

6 ku duwatsu, kuka yi tsalle kamar raguna, ku tuddai, kamar tumaki?

7 Ki yi rawar jiki, ya duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allah na Yaƙub,

8 wanda ya juye dutse ya zama tafki, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓulan ruwa.

Everything we make is available for free because of a generous community of supporters.

Donate